Listen

Description

A duk lokacin da aka ɗaura aure, wata addu’a da ’yan uwa da abokan arziki kan yi ita ce “Allah Ya kawo ƙazantar ɗaki”.


 A al’adance, ɗaya daga cikin manyan dalilan yin aure shi ne samun haihuwa. 
 Sai dai a wasu lokuta, wasu mazan kan nuna a fili ba su da muradin hakan.


 Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan waɗannan mazan da ba sa son haihuwa da kuma dalilan su.