Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ce 'yan haramtacciyar kungiyar aware ta IPOB ne ke bankawa ofisoshin Hukumar Zabe Ta Najeriya INEC wuta a Kudancin Najeriya.
Shin mene ne yasa ake ci gaba da kone ofisoshin INEC a Kudancin Najeriya, kuma wane irin tasiri hakan zai yi ga yankin a zaben 2023?
Shirin Najeriya A Yau ya bi diddigin wannan batu, ya kuma tattauna da hukumar INEC da masana domin gano bakin zaren.