Listen

Description

Zarah na ganin Bama garin al'umma ne mai cike da ban tsoro. A baya, garin ya taba zama cibiyar kasuwanci a jihar Borno. Amma yanzu ya zama tarihi bayan hare-haren da 'yan ta'adda ke kaiwa sama da shekaru goma da suka wuce. Duk da tserewa da ta yi daga sacewa da cin zarafi  daga kungiyoyin 'yan ta'adda, amma yanzu yanayi ya tilastawa wannan budurwa komawa garin da ya tara mata bakin ciki hade da rushewar burikanta. Duk da haka, ba ta tsaya da neman ilimi ba. 

Mai gabatarwa: Zubaida Baba Ibrahim

Marubuciya:Tracy-Allen Ezechukwu

Muryoyin shiri: Khadija Gidado

Fassara: Ruqayya Saeed

Edita: Aliyu Dahiru 

Furodusa: Khadija Gidado

Babban Furodusa: Anthony Asemota

Babban Mashiryi: Ahmad Salkida