Look for any podcast host, guest or anyone
Showing episodes and shows of

Ibrahim & Kai

Shows

Najeriya a YauNajeriya a YauShin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?Send us a textJam’iyyar NNPP wadda Dr. Boniface Aniebonam ya kafa a shekarar 2001, ta samu karfi sosai a Jihar Kano bayan tsohon gwamna Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya shiga cikinta a shekarar 2022 tare da mabiyansa na Kwankwasiyya. Shigowarsa ta farfado da jam’iyyar, inda ta samu gagarumar nasara a zaɓen 2023 ta hanyar lashe kujerar gwamna da wasu kujerun majalisa. Sai dai rikicin cikin gida da rikice-rikicen shugabanci suna ma jamiyyar rauni wanda hakan ya haddasa ficewar wasu manyan ‘ya’yanta zuwa APC, lamarin da ke haifar da tambaya kan makomar NNPP a Kano...2025-05-1624 minNajeriya a YauNajeriya a YauSabbin Dabarun Hana Matasa Aikata LaifuffukaSend us a textMasu iya magana kan ce banza ba ta kai zomo kasuwa. Mai yiwuwa hakan ne ya sa matasan da ake zargi da aikata manyan laifuffuka shiga ofishin ’yan sanda, su kuma fita ba tare da wani ya harare su ba, balle ya kama su.’Yan sandan dai sun ce wannan wata dabara ce ta yakar aikata manyan laifuka irin su sata da fashi da makami da kwacen waya da fyade kai har ma da satar mutane don kudin fansa a tsakanin matasa.Ko yaya wannan dabara take...2025-04-1825 minNajeriya a YauNajeriya a YauDalilan "Farfaɗowar Boko Haram" A Jihar BornoSend us a textA yanzu haka al’ummar Borno na cikin zulumi sakamakon wasu hare-haren da ake zargin kungiyar Boko Haram ce ta kai a wasu sassan jihar. Wadannan hare-hare dai suna faruwa ne bayan shekaru da dama da ikirarin Gwamnati na cewa an yi nasarar nakasa kungiyar.Ko mene ne dalilin sake farfadowar kungiyar ta Boko Haram a wannan lokaci?Wannan ne batun shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.2025-04-1430 minNajeriya a YauNajeriya a YauYadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Kasa KiranyeSend us a textMulkin demokradiyya kamar yadda Hausawa ke cewa ‘yancin dan adam.A lokacin da ta baka damar tsayawa don a zabe ka kan wani mukami, kazalika ta baka damar zaben wanda kake so ya shugabance ka kuma ya wakilce ka.Wani abun da demokradiyyar ta baiwa alumma dama a kai kuma shine na yin kiranye ga wakilan da suka zaba musamman idan wadannan wakilan basa biya musu bukatun da suka tura su a kai.Tuni dai alummar kogi ta tsakiya suka fara kada kuri’un kiranye ga sanatar da suka...2025-03-2530 minNajeriya a YauNajeriya a YauHar Yanzu Akwai Masu Rufin Asiri A Najeriya?Send us a textA tsakanin al’umma akan karkasa mutane gida-gida a bisa mizani na tattalin arziki, musamman a tsarin jari-hujja: akwai mawadata, akwai matalauta.A tsakanin al’umma akwai aji na mutane masu matsakaicin samu wanda ake kira “Middle Class”.Akan saka mutane a wannan aji ne galibi bisa la’akari da aiki ko sana’ar da suke yi, da kudin da suke samu, da matakin ilimin da suka kai, da ma matsayinsu a tsakanin al’umma.Sai dai a baya-bayan nan irin wadannan muntane sun bi sahun matalauta wajen korafi game da...2025-02-1025 minNajeriya a YauNajeriya a YauDalilin Faduwar Farashin Tumatur A KasuwaSend us a textShin mene ne dalilin faɗuwar farashin tumatir warwar a kasuwa? Idan ba a manta ba, a watannin baya farashin Tumatur yayi tashin gwauron zabo wanda aka dade ba’a ga irin sa ba.A wancan lokacin, sai da farashin tumaturin ya kai ga iyalai da dama sun hakura dashi sun koma sayen na gwangwani ko na leda. Wannan ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin zai yi nazari a kai.2025-02-0727 minNajeriya a YauNajeriya a YauYadda "Sojoji Suka Kashe Farar Hula" A Karo Na Biyu A Wata GudaSend us a textBayanai na kara bayyana game da wani hari da Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta kai a kan wasu kauyuka biyu na Karamar Hukumar Maradun ta Jihar Zamfara, wanda ya yi sanadin mutuwar farar hula akalla 15.Wadanda suka shaida faruwar lamarin dai sun ce sojojin sun kai hari da jirgi mai saukar ungulu ne a kauyukan biyu wadanda ’yan bindiga suka kaiwa hari .Wannan na zuwa ne makonni kusan uku bayan da Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta kai wani harin irin wannan a Karamar Hukumar Silame dake ji...2025-01-1324 minNajeriya a YauNajeriya a YauHalin Da Matsalar Tsaro Ya Jefa Wasu Alummomin Arewa A Shekarar 2024Send us a textA cikin ‘yan shekarun nan, matsalar tsaro ta kasance babbar kalubale a Arewacin Najeriya. Musamman a jihohin Kaduna, Zamfara, Katsina da kuma jihar Sakkwato. Daga matsalar ‘yan fashi zuwa ta’addanci, yankin ya fuskanci barazanar tsaro daban daban.Duk da irin wadannan kalubale, mutanen wadannan yankuna sun nemo wasu hanyoyi daban-daban na jure irin wadannan matsaloli. Taimakon ‘yan sa kai a wasu al’ummomi ya taka muhimmiyar rawa, inda kungiyoyin sa-kai da kuma tsare-tsaren gwamnati suka yi tasiri a wasu wurare.Shirin Najeriya A Yau zai yi Naz...2025-01-0222 minNajeriya a YauNajeriya a YauYadda Takkadama Ta Kanannande Siyasar Kananan Hukumomi A Shekarar 2024Send us a textZabukan Kananan hukumomi na cikin al’amuran da suka dauki hankali a fagen siyasar Najeriya a shekarar 2024.Duk da an gudanar da zabukan cike gurbi a wasu daga cikin jihohin Najeriya, zabukan kananan hukumomi na cikin batutuwan da ’yan Najeriya suka fi zantawa a kai, mai yiwuwa saboda ganin da ake yi cewa wadannan zabukan sun fi shafar alumma kai tsaye.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi waiwaye a kan kurar da wasu daga cikin zabubbukan kananan hukumomi suka tayar a 20242024-12-3125 minNajeriya a YauNajeriya a YauGaskiyar Lamari Game Da Harin Sojoji Kan Al’umma A SakkwatoSend us a textA baya bayan nan ana cigaba da samun hare hare da sojoji ke kaiwa kan fararen hula kamar yadda wasu suka bayyana.Ko A shekarar da ta gabata, rundunar sojin kasar nan ta kai wani hari garin Tudun biri dake karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna inda harin yayi sanadiyyar mutuwar gomman mutane.Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zaiyi duba ne kan harin da rundunar sojin kasar nan ta kai a jihar Sakkwato 2024-12-2721 minNajeriya a YauNajeriya a YauTasirin Rancen Naira Tiriliyan 138 A Rayuwar ’Yan NajeriyaSend us a textBayan  da Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu karbo wani sabon rance na sama da Naira tiriliyan daya, yawan bashin da ake bin Najeriya ya kai matakin da bai taba kaiwa ba a tarihi. Da wannan amincewa dai yawan bashin da ake bin Najeriya ya kai Naira tiriliyan 138!Wannan shirin na Najeriya a Yau zai yi bincike ne a kan tasirin da wannan bashi yake da shi a rayuwar ’yan Najeriya.2024-11-2231 minNajeriya a YauNajeriya a YauAbin Da Ya Kamata A Yi Da Kananan Yara Masu Zanga-ZangaSend us a textGurfanar da yaran nan da aka kama watanni uku da suka gabata yayin zanga-zangar ‘#EndBadGovernance’ na ci gaba da yamutsa hazo a Najeriya.Mutane da dama dai, musamman a Arewa, suna ta tofin Allah-tsine a kan kamen yaran, wadanda wasu suke cewa kanana ne, shekarunsu ba su kai a kama su ba ballantana a kai su gaban kotu.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai tattauna ne kan tanadin doka game da kamen kananan yara, da kulle su, da kuma gurfanar da su gaban kuliya.2024-11-0427 minNajeriya a YauNajeriya a YauMe Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Shaukin Ranar Samun ’Yancin Kai?Send us a textA duk lokacin da bikin tunawa da Ranar Samun ’Yancin Kai ya zagayo, bisa al’ada, akan ga ’yan Najeriya suna farin ciki.Sai dai a wannan karon alamu na nuna abin ya sauya; ba kamar yadda aka saba gani a shekarun da suka gabata ba, mutane da dam aba su ma san ana yi ba.Shirin Najeriya A Yau zai yi duba ne kan dalilan da suka sa ’yan Najeriya ba sa shauki kamar yadda aka saba gani a da.2024-10-0126 minNajeriya a YauNajeriya a YauAbin Da Ya Sa Ake Ƙara Wa ‘Yan Band A Kuɗin Wutar LantarkiSend us a textZuwa yanzu masu shan wutar lantarki da ke tsarin Band A sun samu sanarwar kara kudin wutar lantarkiSai dai wasu na ganin ba a iya biyan bukatun da wannan kari ba zai samu muhalli ba Shirin Najeriya a Yau zai tattauna ne kan Dalilin da ya sa ake kara wa masu tsarin Band A kudin lantarki a kai a kai.2024-07-0517 minNajeriya a YauNajeriya a YauHanyoyin Haɗa Kan 'Yan Najeriya Ta Wasan ƘwalloSend us a textFaɗin ƙasa da yawan kabilun da ke Najeriya sun sa zaman 'yan ƙasar uwa ɗaya uba ɗaya masu ƙawazucin juna gagara tun samun ƴancin kai. Ko kun san hanyoyin da ya kamata abi domin haɗa kan ƴan ƙasar wuri guda masu so da ƙaunar juna domin ciyar da ƙasar gaba ta hanyar ƙwallon ƙafa? Lura da goyon baya da fatan alkhairin da 'yan Najeriya suka nuna wa tawagar ƙwallon ƙafar Najeriya a gasar AFCON, mun dubi hanyoyin da za a bi domin samar da ƴan kasa masu haɗin kai da ƙawazu2024-02-1215 minNajeriya a YauNajeriya a YauAFCON: Yadda Za Ku Kauce Wa Bugun Zuciya Yayin Kallon KwalloSend us a textRahotanni sun tabbatar da mutuwar 'yan Najeriya uku sakamakon firgita da suka yi bayan an baiwa kungiyar kwallon kafar kasar bugun da ga kai sai mai tsaron gida yayin wasan su da takwararta ta Afirika ta Kudu. Mene ne ke sanya zuciya bugawa har ta kai ga ajali ko mummunan jinya?Mun binciko yadda wadannan bayin Allah suka gamu da ajalinsu yayin kallon wasan, mun kuma ji ta bakin wani likita kan hanyoyin kaucewa bugun zuciya.2024-02-0914 minNajeriya a YauNajeriya a YauYadda Wata Mata Ta Haihu A Kofar Gida A Mangu Saboda Yaki Bayan Dokar Hana FitaSend us a textHukumomi a Jihar Filato sun bayyana saka dokar ta baci sakamakon rikicin kabilanci da ya rikide ya koma na addini a karamara Hukumar Mangu  amma mahara sun ci gaba da kai hare-hare. Mene ne abin da ya sa har yanzu ba a daina kai hari a Mangu ba? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya binciko halin da ake ciki. ku biyo mu sannu a hankali. 2024-01-2514 minNajeriya a YauNajeriya a YauMakomar Ministar Jinkai Betta Edu Da Shugabar NSIP Halima ShehuSend us a textTun bayan dakatar da ministar jin kai ta Najeriya Betta Edu a jiya Litinin 8 ga Janairu da kuma Halima Shehu daga matsayin  shugabar hukumar bada tallafin dogaro da kai ta kasa kwanaki 6 tsakani 'yan Najeriya sun fara bin kwakkwafin wane hali su ke ciki, kuma mene ne abin da ya sa aka dakatar da su? Shirin Najeriya A Yau ya binciko cikakken abin da ake zarginsu, ya kuma ji ta bakin masanin shari'a kan makomar wanda ya aikata abin da ake zarginsu da shi.   2024-01-0913 minNajeriya a YauNajeriya a YauWane Mataki Ya Kamata Mutum Ya Kai Kafin Shekara 30Send us a textShin kun taba tambayar kanku matsayin da ya kamata matashin da bai wuce shekara 30 ya taka?Da zarar shekaru sun ja ana sa ran a cimma wani buri na rayuwa da zai sa a kalli cewa mutum ya fara samun cigaba da zama cikakken mutum.Shirin Najeriya a Yau ya duba matakin da ya kamata a ce mutum ya kai kafin cika shekara talatin a rayuwa.2023-12-0714 minNajeriya a YauNajeriya a YauDalilin Dawowar Hare-Haren ’Yan Ta’adda A Arewa Maso GabasSend us a textAna murna da raguwar hare-haren 'yan ta'adda a yankin Arewa maso gabas, sai ga shi wasu alamu na nuna akwai yiwuwar wasu na shirin dawo da hannun agogo baya.A 'yan kwanakin nan an samu barazanar kai hare-hare da wasu bayanan sirri a yankunan da ake ganin an ci ƙarfin 'yan ta'addan.Shirin Najeriya a Yau ya duba yadda 'yan ta'adda ke yunƙurin dawo da kai hare-hare a yankin arewa maso gabashin Najeriya.2023-11-0713 minNajeriya a YauNajeriya a YauAbin Da Ya Sa Hisba Ta Yi Kame A KanoSend us a textRahotanni daga Jihar Kano sun bayyana cewa Hukumar HISBA ta kai samame wani hotel da kuma wasu gidaje a jihar. Ko mene ne abin da ya sa hukumar HISBA kai wannan samame a wannan lokaci? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya binciko abin da ya sa HISBA ta dauki wannan mataki a yanzu. 2023-11-0214 minNajeriya a YauNajeriya a YauYadda Mazauna Iyakar Najeriya Da Nijar Suka Shiga Ha’ula’i Bayan Rufe BodaSend us a text’Yan Najeriya mazauna yankunan da ke iyakar kasar Jamhuriyar Nijar na dandana kudarsu sakamakon tsadar rayuwa da tashin gwauron zabon kayan masarufi, tun bayan rufe bodar da Najeriya ta yi a watan Agusta.Anya wannan rufe boda da Kungiyar ECOWAS ta sa aka yi, ba za a ci kai da kai ba?Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya ziyarci garin Illela a Jihar Sakkwato da Maigatari a Jihar Jigawa, da kuma Kwangalam da Jibiya a Jihar Katsina, domin jin halin da mazauna garuruwan suka tsinci kansu a ts...2023-10-1914 minNajeriya a YauNajeriya a YauGwagwarmayar June 12 A Dimokuradiyyar NajeriyaSend us a textYau rana ce ta demukradiyya a fadin kasar Najeriya, wato goma sha biyu ga watan Yuni da kowa ya sani da June 12.An sha fama da gwagwarmaya kafin a kai ga yin zabubbukan ranar 12 ga watan Yunin shekarar 1993 da gwamnatin mulkin  soja ta Ibrahim Badamasi Babangida ta soke.Shirin Najeriya a Yau ya tattauna da masanin harkokin siyasa da ya yi cikaken bayani tare da bayar da tarihin abinda ya faru.A yi sauraro lafiya.2023-06-1215 minFilmmaker Wannabees PodcastFilmmaker Wannabees PodcastS02 #58 Why YouTubers Outshine Brands in Holding Attention?Back in the day, in the age of television. Brands and advertising companies Held the attention, they were the gate keepers and had the power. In today’s world, things are a little different. The power has shifted to the hands of the creators, YouTubers, Instagrammers & Tiktokers. What has caused this shift? How can brands take advantage of that? And what are they missing out on? 2023-04-2023 minFilmmaker Wannabees PodcastFilmmaker Wannabees PodcastS02 #57 Behind The Scenes: Keys to Great Producing In Film and Commercials W/ Karim GadWe were fortunate to have Karim Gad on this episode, an avid and experienced producer in Qatar. To talk about it all. The journey, the setbacks, the wins, the fun along the ride and the lessons. Key aspects of producing. We answer lots of questions like what is the difference between a production manager and a producer? What makes a good producer? How do you maintain a sustainable career as a producer? And lots of fun and interesting stories. Please tune in till the...2023-04-1249 minFilmmaker Wannabees PodcastFilmmaker Wannabees PodcastS02 #56 Here's Why You Shouldn't Make Your Video Ads Look PerfectToday we will be talking about a few thoughts on why making a video ad look perfect could potentially harm your brand. We will discuss our definition of a perfect looking video ad, as well as the times when we must make a video look perfect, super clean and polished.2023-04-0618 minFilmmaker Wannabees PodcastFilmmaker Wannabees PodcastS02 #55 How is Artificial Intelligence Manipulating Truth in Real Time?What is real? Daily tools and devices that we use in our lives are manipulating truth without us knowing. So, can we depend on them? Years down the road, when AI has captured and recorded us in perfect and beautiful shapes, how will that impact the next generation? What does this mean for the average filmmaker? Some thought provoking questions that we try to explore in this episode. Hope you enjoy it! 2023-03-2918 minFilmmaker Wannabees PodcastFilmmaker Wannabees PodcastS02 #54 Limiting Beliefs Filmmakers haveIn this week's episode, we talk about some of the limiting beliefs that we had as filmmakers when we first started out. We also discuss some trends and ideas that hinder filmmakers from moving forward.2023-03-2229 minFilmmaker Wannabees PodcastFilmmaker Wannabees PodcastS02 #53 Chat GPT: Filmmakers Perspective & DiscussionHello everyone! We are Back! Season two of the podcast with new structure, new topics and fresh perspectives. Today's episode is about the one and only Chat GPT and a little bit of it's likes of AI Softwares. In what ways have they changed the filmmaking industry? What does this wave of AI mean for the average filmmaker? And what can utilise them for? Hope enjoy the discussion and many more are on the way!2023-03-1524 minNajeriya a YauNajeriya a YauFadi-Tashin Gwamnoni Don Cin Zaben 2023Send us a textGwamnonin da jam’iyyunsu ba su kai bantensu a jihoinsu ba a zaben shugaban kasa na fadi-tashin ganin ba a maimaita hakan ba a zaben gwamna da za a yi Ranar Asabar 11 ga Maris. Anya wannan farga da gwamnonin suka yi bazata zama fargar jaji ba? Shirin Najeriya A Yau ya dubi yadda gwamnonin da jam’iyyarsu ta fadi a jihohinsu a zaben shugaban kasa ke tunkarar zaben gwamna da ke tafe idan Allah Ya kai mu. 2023-03-0915 min